Abuja
Abuja
Abuja
Abuja
Abuja
Abuja
Yau juma'a,29 ga watan Octoba ne,dubban 'yan shi'a mabiya Sheikh Ibrahim Zakzaky sun gudanar da muzahara mai taken "Labbaika Ya Husain,Free Zakzaky" a garin Abuja. An fara muzaharan ne da misalin karfe uku na rana agogon Nijeriya. Babban maqasudin muzaharan shine tunawa da sadaukarwan Imam Husain (as) a Karbala,wadda albarkacin wannan sadaukarwan ne addinin musulunci ya samu izza da dawwama.Sannan sun yi amfani da wannan daman wajen kira ga gwamnatin Nijeriya da ta mutumta umurnin kotu ta saki jagoran harkar musulunci a Nijeriya,Sheikh Ibrahim Zakzaky. Sheikh Abdullahi Zango ne jagoranci muzaharan,kuma yayi kira ga gwamnati da gaggauta sakin Sheikh Zakzaky a lokacin da yake bayani bayan kammala muzaharan.